Dan iskar da aka samu kwana biyu ba tare da anyi ruwa ba yasanya garin yin zafi, wannan yasa da yawan mazan unguwar firfitowa kama daga matasa har dama maginta ko ina ka bi cikin unguwar maza zaka gani wasu bisa bencina wasu bisa tabarmi kowa da abinda yake, can gefen kwata bakin wani kanti bencin su Muktar ne shida abokan sa da suke zaune gefen teburin da Ibrahim ke saida kaza soyayyiya, kilishi, da dambun nama.
Nasir da ya ƙara so wurin ɗauke da katuwar baƙar leda ne ya zauna ƙarshen bencin tare da faɗin "wash! Allah. . .