Anwar yana office kansa a duƙi yana duba fayel Hafiz ya shigo kallon shi ya yi cikin mamaki "ikon Allah wata sabon gani yau kai ne a office ɗina?"
Sake haɗe rai Hafiz ya yi Anwar ya yi dariya "to Malam soja taimaka ka zauna."
Jan kujera ya yi ya zauna "kwana biyu gaba ɗaya ka manta da ni idan na kira ka ba ka ɗagawa na zo office ɗin ka ba ka nan ina fatan dai lafiya ce ta ɓoye ka?"
"Ina cikin uzurika ne shi yasa. Magana na zo za mu yi."
"To ina saurarin ka. . .
I want to see your information
Allah ya Kara basira