Hannu tasa tana share hawayen fuskarta tana ƙoƙarin haɗiye kukan da ƙyar ta iya danni kukan da take ta tura ƙofa cikin sa'a ta samu ƙofar a buɗe, kutsa kanta ta yi ciki ta tarar da Zhara na bacci tausayinta ya cika ma ta zuciya da sauri ta juya tana tushe bakinta ta fito ɗakin tana kuka. Ɗakinta ta koma ta kira wayar Anwar tana kuka ta faɗa masa abin da yake faruwa ta ƙara da cewa "ba zan iya faɗa ma ta ba don Allah ka zo da kan ka" cikin kaɗuwa. . .