Skip to content
Part 32 of 34 in the Series Kyautar Zuciya by Bilkisu H. Muhammad

Tuni ta dade da farkawa ta takure a  bakin gado kuka take faman yi kewar iyayenta take yi tunda take bata taba kwana a wani guba kukan tane ya farkar dashi da gudu ya mike tare da matsowa kusa da ita.

Nurat Mai ke faruwa?

“Ammina.

ya rike hannunta Yana wasa da yatsunta

“Kiyi hakuri muyi sallah zan kaiki gun su kinji,tashi muje kiyi alwala kinga za,a tada sallah “

ya kamo hannunta bai saketaba har sai da ya danganata ga toilet sannan ya rufe ya barta aciki Shima ya nufi toilet din dakinsa ya daura tasa alwalar ya nufi masallaci

Acan masalaccin dukkan ganawarsa na godiya ne da fatan samun zama lafiya da zuri,a na gari.

Bai komo gidaba sai karfe shida

Gaba daya ta birkita dakin tana neman kayanta donta cire kayan baccin jikinta  ya danni cikin dakin da sauri ta kai hannu zata dauki hijabin da tayi sallah dashi ya rigata dauka yana tsokanarta.

“Kinfi kyau ahaka pls ki zauna a haka kinji zan kawo miki kayan da Zaki saka idan zamu fita.”

“kayi hakuri dan Allah.”

“No,nifa mijin kina Zaki zauna ne ahaka kin

Ji kawai sai ta tina kalamen dad .

Ahankali tace

“To zanyi yadda kakeso .”

“good my baby.

Ya matso jikinta sosai yanayi mata rada.

“Yanzu gaya mini Mai kikeson ci?

“Na koshi.”

dungure mata kai yayi cikin salon wasa .

“Ke kin Isa ki zauna da yunwa alhalin akwai bebina atare da ke kawai ta sunkuyi da Kai cike da kunkya.”

“Ina zuwa.”

ya fice har kusan karfe takwas da rabi bai dawoba ta fara kaguwa da tsoro tana iya jin hayaniyar ma aikatan gidan ta dauko alkur,ani ta soma karatu karfe tara ya shigo rike da wata katuwar leda.

Suna hana ido ya saki ledar kasa ya bude hannayenta alamar ta toho a kunyace ta karaso ta fada faffadan kirjinsa ya maida hannu ya rufe ruf sun dade ahaka yana jin wani irin nutsuwa na ratsashi sannan ya rabata da jikinsa Yana janye da hannunta har zuwa dakin gado ya zaunar da ita .

“Kinyi wanka?

Ta kada kai alamar eh.

“Ok to taso muje ki shirya sai mu karya mutafi gun dad ko.”

Yana rike da hannunta wani daki ya kaita wanda gaba dayansa kayan kyalakyalen mata ne aciki .

Ya dubeta.

“Zaki iya ko sai na taimaka Miki .

ya karaso jikinta sosai Wai zai cire mata riga sai ga kwalla shar,shar da sauri ya dauke hannunsa.

“Allah ya baki hakuri,afito lafiya ga kayan da Zaki saka nan sarkin kuka.

Yaddafurta maganar ne yasata murmushi ya Kai hannu yaja hancinta sannan ya fita ya janyo mata kofar.

har yagama shirinsa baby alamunta hakane yasa shi komawa dakin ya taddata kwance a gado tana bacci ya zauna kusa da ita ya kafeta da idanunsa ahankali ta bude ido ta zabura ganinshi zaune kusa da ita.

“Jiya bakiyi bacci ba ko,ok to bara na kullo mana kofar sai muyi baccin ko.

duk kunya ya gama kamata.

“kayi hakuri yanzu zan shirya kabani minti uku.”

ya duba agogon dake daure a tsintsiyar hannunsa .

“Shikenan baki da matsala .*

Ya juya ya fita

Nurat yarinya ce Mai sanyi aikin awa daya sai tayi awa biyu tanayi.

Ya sake turo kofar dai dai lokacin da take kokarin saka doguwar riga tayi saurin durkusawa yana murmushi ya matso kusa da ita ya dagota.

“matata ki tsaya a haka nayita kallonki,kada ki matsa idanuna suna son ganin wannan kyakkyawar halittar taki”

yasa hannu ya shafi labbanta masu laushi da sulbi ahankali cikin dabara ya matso da nasa bakin kusa da nata batai aune ba kawai taji harshensa cikin bakinta kawai ta rintse ido haka ya shiga bida ita har sai da ya kaita kasa ita Kuma tsoro ya hanata yin kwakkwarar motsi yagama sarrafata son ransa dan kansa ya kyaleta .

ta kasa hada ido dashi fahimtar hakane yasa shi ya fita ya koma darning room yana jiranta nan ma bata fitoba dole ya koma tana bakin kofa tana tinanin ta yadda zata iya hada idanu dashi ahaka ya risketa batare da yace da ita komiba ya roko hannunta sukayi waje

acan da kyar taci abincin sai da taga da gaske idan bata ciba bazasu je gun abban nataba sannan ta dan caccaka.

Suna fitowa harabar gidan ma,aikatan gidan suka dinga zuwa suna gaisuwa yana kuma gabatar musu da ita ,addu,a kuwa sunshashi har zuwa ma,ajiyar motoci motar da suka shiga ya gama haduwa bata taba ganin irinsaba .

***.                        ***.                     ***

tunda suka shiga unguwar basu ci karo da karamin gidaba irin maka makan gidajennan ne gida Mai lamba goma sha biyu shine gidan gidan da yafi ko wanne kyau da girma, horn yayi Mai gadi ya bude tare da danna hancin motar cikin harabar,ashe a tawajen gidan ba,aga komiba daular na ciki .

wani sojane yazo yayi musu jagora zuwa wani tamgamemen setting room Mai kama da filin ball sabida fadi

Nurat ta hangi dad dinta da gudu ta nufeshu kamar Yar baby ta fada jikinsa.

” dad ina ammina meya sameta?

“babu abunda ya sameta tananan kalau .

deedat ya durkusa cikin girmamawa ya gaidashi sa annan ya nemi guri ya zauna,Alhaji munir tare da atiku sai ummin deedat bai San sa,ar da ya mike tsaye hadi da tarar taba.

“ammina Mai ya kawoki nan?

bata ce komiba ta kamoshi ta zaunar .ta koma ta janyo Nurat ta rungume.

“Kece surukar tawa?

Cike da kunkya  Nurat ta sunkuyi da Kai.

“yarona baka gaida mahaifin nakaba.”

ras gabansa ya buga ya dago kai da sauri Yana dubansa.

Alhaji munir ya taso yazo ya dago deedat ya rungume yana Mai zubda kwallah.

“Naso ace mutumin kirki irinka na sameshine ta hanyar halas Allah ya yi mini babban kyauta sai dai ta haram tacciyar hanya ne,yarona kayi mini afuwa ban taba aikata kuskuren yin zina ba wannan wata jarrabawar ce daga ubangijinmu sai dai na godewa Allah Dana zamto nine silar doraka akan duk wata rayuwar wadata Ina son ka dauka haka Allah ya tsara maka.

Kuka ya kwace masa wani irin sonsa da kwanarsa ya dinga ratsa deedat,kallo daya zakayi masa ka San Yana da Kamala,

“abbana bakayi min komiba kada ka kara neman yafiyata nine zan nemi yafiyarka da ban nemekaba.

Ya juya ga umminsa adokance.

“Kece Kika nemo minshi.

Alhaji atiku yayi murmushi.

umminka tazama matar abbanka.

“ta Yaya hakan ya kasance?

” hukuncin Allah kenan.

Deedat yadingajin kansa kamar sabon mutum ya Sami farin ciki a lokaci daya yasami ummi Abba da mata.ganin komi yakeyi tamkar a mafarki.

Alhaji munir ya dubi daddy .

“Ranka ya ga dan naka ya karaso kace kana da abincewa “

daddy ya soma magana.

“da farko Ina alfahari da diyata ta zamo daya daga cikin dangin nan,inama ace zanci gaba da rayuwa danayi farin cikin haduwa da sababbin abokai yadda dangina suka gujeni nasani ku bazaku kyamaceniba.”

“dad Mai kake cewa ne.?

*Nuratu zan gaya Miki dalili,sai dai Ina Jin tsoro kada kiyi dana sanin kasancewa na mahaifinki.

ta rike hannunsa sosai tana kuka.

“Ko Mai kayi ko ya kake bazan taba yin Dana sanin kasancewar  ka babana ba koda Mai ka aikata zanyi alfahari da Kai Ina tare da Kai.”

yayi murmushi mai ciwo.

” Kada kiyi saurin yanke hukunci kibari nafara baki labarin kaina.

Gaba daya suka tattara hankalinsu kansa ita kuwa Nuratu gaba daya ta shiga zulumi,yayinda deedat ya faki ido ya danna recording .

“Tin Ina yaro ni ba wani mai galihu bane iyayena sun rasu tin Ina dan karami,haka dangina basu damu dayadda nake rayuwata ba naci banciba babu ruwansa a,irin wannan rayuwar na taso har girmana ,bani da taka maimai sana,ar yi yadda “yen uwana suka gujeni ne na cire araina Ina da wasu dangi Dan haka na tashi daga mahaifata na komo jos ananne muka hadu da mahaiyarki itama dai bata da wani gata ahannun kakarta take soyayya Mai karfi ya shiga tsakaninmu da ita bamuwa iya wuni batare da munga junan muba har mun fara tinanin yadda zan Sami sana,aryi har muyi aure cikin wannan hali Mahaifiyarki ta hadu da wani hamshakin mai kudi sai dai Sam bata bashi hadin kaiba sabida soyayyata.

wata rana muna hira a kofar gidansu wata lafiyayyiyar mota tayi parking agabanmu amminku take fanamin shine wannan da sauri nace da ita tace ni yayan tane haka ko akayi tashi daya ya dauki dubu dari ya bani nayi kamar zanyi hauka dan bantaba rike dubu uku na kaina ba nan fa nashiga lallashin ta akan ta aureshi idan muka gama tatsarsa sai ta kashe auren muyi auren mu nasha wahala kafin ta amince ai kuwa ba,a dauki wani lokaciba akayi auren duk da haka bamu daina soyayya ba zanzo gidanta azuwan Yayan tane zamu wuni muna hira lokaci kankani amminku ta sauya Ina nufin kyawunta ya fito sosai kyauwunda ni kaina bansan tana dashiba nanfa kishi ya motsa kullim Ina tinanin ta Yaya zanyi na rabata da gidan Kuma duk wannan son da takeyi mini ban taba take taba Ina nufin kusantarta Ina yunkurin aikata sai dai bata bani hadin Kai.

Lokaci daya naga cikinta na girma Wai ashe cikine da ita hankalina ya kara tashi mukayi ta rigima da ita akan cewar sai tabashi guba cikin abinci yamutu amman fir taki hakan yasa nayi mata yaji kusan wata guda ban jeba Killin faman kirana takeyi ban daukar wayar duk kuwa da yadda sonta ke Kara karuwa araina rannan kawai sai naje gidan inda tayi mun alkawari zatayi yadda nakeso amman in bari ta haihu na amince mata da hakan

bayan ta haifi Aazeem da kwana arba,in na sauka agidan da guba poison tagama abincin rana na bata nace ta zuba masa tace zata zuba na yadda da ita na samu gu na labe alokacinda na ji kugin motarsa Ina kallon ta ta dauki abincin ta Kai ta jere a darning room ta komo ta dauko maganin ta cilla a shara na lallaba na je na dauko tashiga dakinsa na fito na shiga darning room din na bude abincin na zuba .

Ina labe suka fito tare ta zuba masa abincin Yana faraci ya soma tari bakinsa na fidda wani irin kumfa kan wani lokaci tini ya fadi rai yayi halinsa nakoyi tsalle na fito daga ma koyata inda na dinga murna Ina fadin Ashe kina Sona gashi kin kasheshi din tanaji tana gani na juya lamarin kanta bata da mafita haka ta amince da itace tayi kisan babu Wanda ya gane kasheshi akayi yan uwansa sukazo akayi masa suttara bayan arba,in na takura mata akan ta dage araba gado haka akayi tsananin son da takeyi min bata iya Musa min inko ma naga rana neman Musa min yanzunnan zanyi mata barazana ince da ita zan gaya wa kowa itace ta kashe mijin nata innayi hakan takan tsorata watansa biyu da rasuwa aka raba gado munsami dukiya na ban mamaki gidaje kadai sai da Aazeem ta mallaki sama da gida ashirin banda kamfani gaba daya muka hada muka siyar tana gama takaba mukayi aure  sannan muka dunguma zuwa kano a inda muka kafa kanmu munsiyi kamfani da gidaje ba,a dadeba muka Sami labarin rasuwar kakarta nan nazamo nice komi nata akano kowa yayi zaton Aazeem yatace bayan shekaru kusan takwas zuwa tara aka haifi Nurat

na bawa yata tarbiya inda sai ka zaci bana kaunarta yayinda na gatanta Aazeem ta gefe Ina kuma lalata rayuwarta akarshede na bude mata ido wannan shine takyitaccen labarina.

Gun yayi shuru sai kukan Nurat ne kawai ke tashi tanajin kunyar dago kai da dad yasani bai bada irin wannan labariba ummin su deedat ta dinga lallashinta tana janyo mata ayoyin alkur,ani.

“Idan Allah yaso zai iya wankeshi tunda yayi nadama,da bayyi nadama ba bazai bayyana surrin Saba.

Yana sharar kwallah ya dubi Nurat.

“Nasani yanzu Zaki kyamaceni ni kaina na tsani kaina burina na bar wannan duniyar nasan Allah bazai taba yafe min ba na cutar da matata na zalinceta yanzu bansan ta Yaya zata kubuta daga gun yansanda ba.

Alhaji munir yace.

dole zamuje ka wanketa idan Kai aka kamaka zamu San yadda zamuyi ka kubuta kaji.

“daddy bazai kubutaba wallahi kasheshi za,ayi duk Wanda ya kashe rai Shima kasheshi akeyi.

Ta rushe da kuka.

“kilama dukanninku kashe ku za a,ayi.

” baza,a kashe suba kidaina razanar dashi komi zaiyi daidai.

Inji deedat

Alhaji munir da atiku sun koma daya falon don su tattauna akan lamarin bayan sun Dan tattauna suka Kira deedat da umminsa da Kuma Nurat yarage sai daddy.

sun gama tattaunawa su sun fito sai dai me babu shi agun sai wasika daya bari

deedat ne ya dauki wasikar ya fara Karan tawa.

Nasani muddin na mika kaina ga yensanda dole zasu kashe nine bayan sun gama nunani a idon duniya ni Kuma bana bukatar haka,Ina son kuyi mini addu,a nayi nadama a rayuwata nayi dana sani ga Nurat nan ku riketa da amana,Allah ya kaddara saduwar mu.

Innalillahi Nurat ta dingayi ta na maimaitawa  Ahaji munir ya ce su shiga nemansa kada yaje inda zai cutar da kansa kokarin barin gidan suke Kira yashigo wayar deedat a inda aka sanar dashi dad yayi mummunan hatsari ko motsawa beyiba rai yayi halinsa .

Wata gigitacciyar kara Nurat ta saka Bata sake sanin inda kanta yakeba.

ta farka ta ganta kwance a cinyar amminsu inda ta rungumeta tana sakeyin kuka  idanunnan da kyar take iya budesu har tayi ramar wuni daya gidan shake da mutane abin mamaki babu alamar kuka ka damuwa a fuskar ta.

“ammi baki damu da daddy ba kenan.?

ta dubeta.

“Mai yasa Kika tambayeni.?

ta rausayar da Kai babu komi .

“bakomi,kawai dai,Amman dai kin yafema daddy ko.

Bata, bata amsaba kawas da Kai tayi.

tasake cewa.

“ammi ya akayi Kika dawo gida.

“dalilin mijinki da surukinki,mijinki ya nadi duk labarin da abban ki ya bashi wannan shine sanadiyar kubutata,Deedat ne dinga kiranta a waya tanajin nauyin dagawa musamman inta Rina da ammi bata sonta da shi ammi na kula da Kiran .

“Wai ke ba mijinki na kiranki ba ,ki daga Kiran Mana.”

ta latsa kure ta Kara a kunne.

“Kina Ina,ko Zaki taimaka min naganki pls .

Ya fada amarairaice.

batace komiba kawai ta katse wayar tanajin nauyin tashi.

“Wai ba kiranki yakeyi bane?

hakane yasa ta mike acan setting room ta sameshi shida Salim tinda ta toho ya kasa dauke ido daga kanta duk da tana cikin yanayin damuwa sai yaga tayi masa kyau sosai.

Samun gu tayi ta zauna akan carpet gaba daya tausayinta yakeji ta rasa mahaifi Mai mutukar sonta,ada Yana Jin haushinsa,Amman a yanzu kaunarsa yakeyi zai ci gaba dayi masa addu,a

Salim ya fara magana cikin muryar lallashi.

“Ya Karin hakurin mu.

ta amsa batare da ta dago kaiba Salim din ya cigaba dayi masa addu tana amsawa da ameen daga bisani ya mike.

“Zan je waje,sai ka fito.

Kanta akasa tana wasa da yatsunta kawai taji hannunsa ajikinta,da sauri ta dago kai suka had a ido ta sunkuyi da Kai kasa kowani daga ido tayi zataga yana kallonta.

<< Kyautar Zuciya 31Kyautar Zuciya 33 >>

Drop a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You cannot copy content of this page.
2
Free daily stories remaining!
×