No.86, Garki 2, Abuja...
RABI POV.
Zaune take daga bakin gadonta tana latsa wayarta. Ta shirya tsaf dan zuwa islamiyyar da Zaid ya ambata mata, yanzu haka shi take jira. Ji ta yi zuciyarta na tashi, hakan ya sa ta aje wayar hannunta. Jin cikinta murɗawa ya sa ta miƙe tsaye, sai kuma ta ji amai, ba shiri ta nufi banɗaki da gudu.
Amai ta shiga yi kamar me shirin amayo hanjinta, duk abun da ta ci na safiyar tas ta zazzage shi. Kuma bayan ta gama aman sai ta ji kasala ta kamata, ta ji. . .