Muhusin ya shigo office ɗin Habib hannunsa riƙe da wasu takardu kallon mamaki yake bin Habib da shi.
Habib ya ɗago yana kallonsa kafin ya ce; "lafiya malam kashigo kayi man tsaye aka kana kallona kamar naci bashinka zan gudu?"
kujera Muhusin yaja ya zauna kafin daga bisani ya ce; "ba dole ba magidanci dakai kabar gidanka kazo waje kana cin abinci."
"Mts! bata jin daɗi ne shiyasa" ya bashi amsa a taƙaice,
"Ah mutumin ko kagama aiki ne?"
Yayi maganar cikin tsokana "kana da matsala daga nace bata da lafiya sai ka kai zancen nawa wani. . .