Skip to content
Part 39 of 64 in the Series Mutum Da Kaddararsa by Maryam Ibrahim Litee

Haka zama na ya cigaba a gidan Aunty Farha, zan yi girki na safe da dare a kullum saboda ya Safwan, gyaran bedroom dinshi ne sai ranar kwana na nake gyarawa zan yi kwalliya irin wadda na ga dama in fito abu na, har na cika wata ɗaya.

Ranar da na cika watan ina zaune a ɗakina da daddare ina rubutu da wata Malama ta samu rubutun kuma yana da matuƙar yawa tunda na yi Isha’i nake zaune.

Ƙarar wayata da ke gefena na ji sai na kai hannu na ɗauko ta na kanga kunnena “Me kike yi har yanzu ina jiran ki?

Na dubi agogo na ɗan rufe baki don ban san lokaci ya tafi haka ba.

Na ce “Note nake.” “Note ya fi mijinki ko?
Ya ce cikin muryar da ta sa na ji wani yar,

“Zan yi wanka.”

Na ce cikin nawa salon da ban san san da na iya shi ba.

Na cillar da pen ɗin na miƙe na kwaɓe kayan jikina na faɗa bathroom na wanke jikina tas na fito na shafa mai da hoda na dan goga wet lips sai na goggoga turarukan Mami, akwai na tsugunno na yi tun da na yi Isha’i.

Sai na samu kaina da bincika kayan da muka sawo da Zainab waɗanda tun zuwa na ban yi amfani da ko ɗaya ba na kasa sanyawa saboda rashin kirkinsu, riga da wando na ciro masu roba kalarsu baƙaƙe rigar tana da dogon hannu sun kama ni sun lafe da fatar jikina na dubi kaina a madubi yayin da nake sanya yankunne masu kamar warwaro, har yau kaina a tsefe yake duk ya ishe ni anya zan iya tsayuwa gaban ya Safwan a haka? Na tambayi kaina daurewa na yi na zura silifas na fita dakin na murza key da Aunty Farha ta kulle ta ciki na fita an kashe komai a falon na shige.

Yana kwance a gadonsa ya tokare bayansa da pillow yana latsa waya daga shi sai wando.
Kallo ɗaya ya tada kai ya yi min sai ya buɗe hannuwansa na taka a hankali na hau gadon na kwantar da kaina bisa ƙirjinsa ya zagaya duka hannuwansa ya rungume ni na ɗago da kaina na saita bakina da nashi na ba shi peck sai na cire na ce “Za ni gidan Mami ka kai ni wajen Mami.”

Bai magana ba kayan jikina ya fara ƙoƙarin cirewa yana raɗa min kalaman da suka sa na rufe idona.

Na ga abin al’ajabi a wurin ya Safwan a wannan dare don hatta Aunty Farha da ta kinkimo ni sai da ya gode mata cikin fitar hayyaci.

Kamar yadda na saba yana tashi don yin wanka ya yi shirin masallaci na gudu na koma ɗakina ina kuma yin Sallah na hakura da komawa barci na fita na hada abin karyawa Iya Larai na gefena tana taimaka min da miƙo wancan ɗauko wancan har na kammala na koma daki.

Lahadi ce ba fita zai yi da wuri ba sai yamma sai na kwanta barcin kusan awa na yi na tashi na yi wanka na shirya yau ma cikin irin kayan jiya ne doguwar riga ita ma mai roba ce don haka ta fidda komai ban sa ɗankwali ba kama gashin kawai na yi ban ga ɗankunnena na daren jiya ba sai daya na dauko na san na baro shi kenan a gadon ya Safwan, wani dogo na ciro na sanya na fita.

Tunda na fito ya Safwan da matarsa da ke zaune suna karyawa suka kalle ni a tare ba kuma wanda ya damu ya kauda idonsa ni kuma na nufe su, gaban tebur ɗin na tsaya na ɗora hannayena sama muna fuskantar juna da ya Safwan Aunty Farha ke gefe na ce “Ina kwana Aunty Farha?

Abincin da ta ɗebo ta kai baki ta ga fitowa ta ta kasa haɗiyewa kuma ba ta fito da shi ba ya sa ta kasa magana ya shaƙe ta take ta kama tari, kafin ogan ya ba ta ruwa na yi saurin tsiyayawa na miƙa mata muna yi mata sannu sai da ta natsa ina nan dai tsaye saitin shi cikin rage murya na ce “Ya Safwan ina son zuwa Sallon kaina ya dame ni.”

Ya dubi aunty Farha “Anjima sai ku je?

Ta ɗaga mishi kai.

Na juya ina kaɗa ƙugu na shige ɗaki.

Shi ma miƙewar ya yi don ya kammala ya shiga wurin shi ya bar Aunty Farha ta rafka tagumi cikin tunani can kamar an tsikare ta ta mike cikin sauri ta bi bayan shi ta samu ya shiga wanka ta zauna zaman jiran shi har ya fito yana cikin shiri sai duban shi take tana jin kishin shi mai tsanani yana ƙara ratsa ta tare da tuna yadda Bilkisu ta fito dole ma yarinyar ta koma inda ta fito.

Ta maida duban ta gare shi ya shirya cikin wata farar shadda da hula da ya yi matuƙar kyau “Dear.” Ya juyo ya dube ta “Uhmm ya kamata Nana ta koma gida, daga ta yi one month.”

Wani shegen kallo ya yi mata “Ai ni ba hannuna, yadda kika ɗauko ta sai ki sanya ta gaba ki mayar da ita.”

Ta yi turus jin amsar da ya ba ta ta shiga kallon gadon kamar shi zai sa ma mata mafita karaf idonta ya faɗa kan ɗan kunne guda ɗaya ta mika hannu ta dauka ƙirjinta na lugude, “Ɗan kunnen waye Dear? Ya dubi ɗankunnen “Wa ke kwana a ɗakin ya bar ɗankunne?

Ta haɗiye miyau sai ta miƙe drawer da idan ta bar ɗankunne yake budewa ya ajiye mata, ta buɗe akwai wani ɗankunnen amma ba irin na hannun shi ba.

Ta juya a sukwane zuwa ɗakinta yankunnayenta ta yi ta dubawa don tana da irin wanda ta ga warin dakin Safwan ɗin

Sai dai ko na tan ba ta gani ba sai ta hakikance na tan ne ta bari.

Wata ƙakkarfar ajiyar zuciya ta sauke ta koma daki ta samu yana sanya links
“Dear.”
Ya waiwayo ya dube ta “Ina jin tashin zuciya da zazzaɓi da rana zan je in ga Dr Sa’a.”

Ya ce “Ki bari mu ga Dr da kike gani.”

Ta girgiza kai “Ni dai don Allah Dear.

Ya yi shiru ta san ya amince kenan “Ba na iya barci a ɗakina Dear ka yi haƙuri in riƙa zuwa nan ɗin.”

Bai ce komai ba sai bundle guda da ya ajiye mata na yan ɗari biyar “Ga shi nan na ce za ku je Sallon da Mami, za ku iya sayen duk abin da kuke bukata na ƙyale ƙyalen ku.”

Ai kusan ruɗewa ta yi da jin sunan Mami da ya kira ita ma Mamin zai riƙa kiran ta don tana da sunan Maminsa tirƙashi!

Ni zan fita wani ke kira na.” Ya ce mata har kuma ya buɗe ƙofar ya fice komai ba ta ce ba sai tagumi da ta rafsa kafin ta miƙe da kuɗinta a hannu zuwa ɗakinta ta yi wanka don haka kwalliyarta ta gyara ta canza shiga da wani tsadadden less da ya amshe ta ya yi mata kyau sai da ta ɗauki hand Bag ɗinta ta tura wa Safwan saƙo da ta je hospital din daga can za ta tafi gidan Aunty Zubaida. (Auntynta da ta riƙe ta)

Gabaɗaya ta kashe wayar tana gama tura sakon don ma kar ya kira ta ya yi zancen zuwa Sallon ta fita cikin takalminta mai azabar tsini ta leƙa kitchen Iya Larai ta kara gaishe ta ta ce “Zan fita idan Oga ya shigo ki sa min ido tsakanin shi da yarinyar nan.”

Iya Larai ta amsa da “In sha Allah Haj.”
Har tana ranƙwafawa ta juya iya Larai ta bi bayanta da kallo ta gatsina baki “Allah ya tsare ni saboda ni ce butulu wannan yarinya mai kirki da mutunci zan wa haka ko jiya kaya ta ba ni ta in kai wa yarana yammata.
Tunda ta zo na samu sauƙin aiki kamar jaka.

Farha da fitarta asibitin da ƙawarta Dr Sa’a ke aiki ta yi wa tsinke tare suka yi karatu duk da kowa da fannin da ya karanta tun suna Sakandire suke tare.

Sai da ta shiga asibitin ta kunna wayarta ta kira ta cikin sa’a kuma ta tabbatar mata tana ciki.

A office ɗinta da take duba marasa lafiya ta same ta sai da ta gama duba matar da ke gaban ta ta fuskanci Farha suka gaisa da kyau da tambayar iyalansu.

Farha ta yatsina baki “Magani na zo ki rubuta min na maganin nauyin barci da kika san ni da shi tun muna makaranta.”

Dariya ta yi Farha kuma ta tsuke fuska “Ke dai banza ce haka kike wa patients din naki?

Ta ƙara dariya “Nauyin barci ai halitta ce ta mutum in ban da abin ki Farha.

Yanzu dai ba maganin da za ki ba ni? Ta ce babu ta dubi agogon da ke kafe a office ɗin “Bari in wuce Sa’a.” Ta mike tana mata rakiya

“Sai na leƙo aiki ne ke riƙe ni.

Sai da ta shiga mota ta juya ciki. Wayarta ta kuma cirowa ta kira ƙanwarta ɗiyar Auntynta ta biyu ta ce

Ta saurare ta tana hanya za su je gidan wata kawar auntyn ta ta da ke shigowa da kaya daga waje za ta duba wasu kaya tana isa ta same ta ita take jira suka tafi a motar Farha.

Bayan gaisawar da suka yi da Hajiyar ta faɗa mata kaya take so English wear ta ce babu matsala an shigo da sababbin kaya wayarta ta ba ta ta zaɓa ta aika shagunanta aka zo da kayan da Farhan ta zaɓa, ta yi mata transfer kudin da ta faɗi na kayan suka fito tare suka ƙara tafiya zuwa gidan auntyn inda Farha ta yi niyyar wuni har dare.

Safwan da ke zaune a Office ɗinsa na General manager na kamfanin motocin nasa suna cinikin wata da mota da mutumin da ya kira shi.

Cikin yaran kamfanin ya kira daya ya ce su fita da mutumin zai ƙara duba motar, jin shigowar saƙo ya duba Farha ce, fita kawai ya yi daga wurin saƙon na ta ya tura wa Bilkisu sakon kar ta cire wannan kwalliyar ta bar mishi zai dawo ya gani hotunan da ya yi mata a mabanbantan lokuta ya buɗe yana gani anya ba abin da Mami ta ba yarinyar nan yake jin abin da yake ji game da ita ya tsaya kan shigar ta ta jiya da daddare wani irin abu ke taso mishi da ya kasa daurewa miƙewa ya yi ya fita zuwa inda ake ganin motar ya ce shi zai wuce mai sayen motar ya biyo shi ganin ya nufi inda motar da ya zo cikin ta take “Alh Safwan da ka tsaya mun karasa.”

Ya yarfa hannu. “Ai mun gama ka sanya kudin kawai.”

Ba abin da za a kara cirewa Haj Safwan?

Murmushin da bai cika yi ba ya yi yana buɗe motar “Iyakar kuɗinta kenan na faɗa maka.”

Ya shiga yana yafuto Bala da ya tura wurin mai sayen ya gaya mishi inda suka tsaya shi zai wuce ya faɗa motar ya bar wurin.

Yana tuƙin yana tunanin yadda ya matsu ya isa gida ya yi ido biyu da ita yarinyar tana rikita shi ba zai iya kwatanta yadda yake jin ta a ranshi ba.

Da komawa ta daki wayata na ɗauko na kira Mamana sai da na gaishe ta da tambayar ƙannena da baban su ta tambayi yadda muke sai na tambayi kasuwancin nasu yadda yake tafiya ta ce
“Kowa lafiya lau, kasuwanci kuma Alhamdulillahi budi kawai muke ta gani ta shiga shi min albarka sai na tuna da Babana yar ƙwalla na share na ce “Akwai kudin sadakina da wasu ma da Baba na Kaduna ya ba ni, an buɗe acc din in turo muku ku kara a shagon?

Ta ce “An buɗe ta cigaba da gaya min aure ɗan hakuri ne ki yi wa mijinki biyayya ki kuma yi haƙur.”

Na ce “To. Muka yi sallama na kira Zainab wadda na ji muryarta kamar ba ta da lafiya na ce kalau dai kike ta Najib?

Ta ce ba ta da lafiya ciki ne. Tsiya na hau yi mata ina faɗin zarin ta ya yi yawa.

Ta ce “Saboda Allah daga ki tausaya min ? Na yi yar dariya “Allah ya raba lafiya.

Ta ce ina ogan da gwana uwar iya?

Na yi dariya duk suna lafiya “Ba matsala kenan?

Na ce “Babu Zainab, sai dai ni bai taɓa ce min yana so na ba in dai ba yana cikin mayen giyar dare ba.”

Ta yi yar dariya “Shi kenan damuwar ki?
Na ce “Ita kenan don duk wata kulawa yana ba ni.”

To ki godewa Allah kawai, sannu sannu watarana zai ce miki.

Na ce “Ina so a riƙa gaya min Zainab.”

Wata dariyar ta ƙara “Zai fadi miki har sai kin gaji da ji, ai kin kai a ce mikin.”

Na ce “Ban son iskanci.”

Jin kamar ana taɓa ƙofar na zuba mata ido ganin shi kuma ya yi matuƙar ba ni mamaki na ce ma Zainab sai anjima na miƙe tsaye ina mishi Sannu da zuwa ya ce “Sai ki saki jikinki dodon taki ba ta nan, ban da alkunya da nake wa Farha da a gabanta zan riƙa zuwa ina daukar ki bakin gadon ya zauna ya dora ni kan ƙafarsa hannuwansa gabaɗaya ya tura cikin rigata da ya sa na kasa zama tsaf ya shiga yamutsani ina mishi shagwaɓa.

Sai da komai ya lafa yana kwance yana mayar da numfashi na ce “Don Allah ka kai ni in ga Mami, ina so kuma in yi kitso don daga shi har Farhan ba wanda ban ga fitar shi ba ta window.

Bai yi magana ba sai janyo ni da ya yi ya ɗora saman jikinsa dole na shiga barci kamar yadda shi ma ya ɗauke shi.

Mun farka ana kiran sallar Azahar a toilet din ɗakina ya yi wanka na je na dauko mishi jallabiya yana fita ni ma na yi zan shiga kitchen ya shigo ya ce in bari in shirya kawai mu fita cikin jin dadi na faɗa daki na shirya ina rataya jaka ya shigo cikin kwalliyar ƙananan kaya da ya yi min kyau kamar kar in daina ganin shi.

Bundle na yan ɗari biyar ya ajiye min ya ce in sayi abin da nake so. Na ɗauka na yi mishi godiya muka fita na leƙa ɗakin iya Larai na yi mata sallama tare da cewa zan fita ban yi girki ba ta shiga kitchen ta samar wa kanta abin da za ta ci da mai gadi.

Bookmark
ClosePlease login

No account yet? Register

Rate the story.

Average: 5 / 5. Rating: 1

As you found it interesting...

Follow us to see more!

<< Mutum Da Kaddararsa 38Mutum Da Kaddararsa 40 >>

Drop a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You cannot copy content of this page.
3
Free daily stories remaining!
×