"Wayyiiiihuhuhuuuuu... jama'a ku saurara, kowacce ƴar abu kaza-kazan uba ta tsaya cak a inda take! an sace jakar uwar amarya cike taf da maƙudan kuɗaɗe..."
Na jiyo wata murya mai tsananin taratsi da hargagi daga can cikin ɗakin uwar bikin tana faɗin haka, a daidai lokacin da na ɗaga cinyar kaza na nufi bakina da nufin yi mata wani yaga na wulaƙanci, irinna an daɗe ba'a gamu ba.
Ƙirjina ne ya yanke ya faɗi rugugum! na ɗaga idanu a tsorace na kalli Fatima, akayi arashi naga ita ɗinma ni take. . .
Hhhh Lallai fa rabon ayi
Muna biye dake. Don mu ji wace tautsayin k kaita ga rabon ayi
Muna biye. Fatan alheri.
#haimanraees
Fatan alkhairi Allah ya kara baseera