Da safiyar Litinin sai farkawa suka yi ba su tarar da Binta ba, dama bai yi niyyar zuwa aiki ba, qiri-qiri yayi niyyar yanka qarya ya bijirewa zuwa aikin, ya dandani zumar zama da Nabila ya ji ba irin wadda za’a bi da ruwan haquri ba ce.
Nabilan ce ta fara zuwa da labarin Binta ba ta nan qarfe takwas bayan ta je gaishe ta, tana neman ta rakito damuwa ya ce mata,
“To menene na fara damuwar ke ba ki kira ta a waya kin ji inda ta je ba?”
Ya je ya dauko mata wayarta ya. . .