Sai da Ummi ta fita tukunna Huda ta fahimci Aslam baya d’akin…har ta fara murna sai kuma ta ji k’arar ruwa a toilet. Kamar mara gaskiya haka ta zauna ta k’ame a guri d’aya har ya fito.
Kallonta kawai yayi ya d’auke kai, ya fita. Sai a sannan ta sauk’e k’akk’arfar ajiyar zuciya sannan ta zabgawa k’ofar da ya bi ya fice harara kafin itama ta mik’e ta shiga toilet d’in tayi alwallah ta fito ta tayar da sallah. Ta jima tana adduar Allah ya dawo da Ya. . .