Skip to content
Part 10 of 30 in the Series Tambaya by Haiman Raees

Wane Irin Da Ne Ni?

Amshi: 

Wane irin ɗa ne ni?

Wane irin ɗa ne ni?

Wane irin ɗa ne ni?

Yaushe ne zan canza? 

01.

Da fari farin farko, na tuno da yarintata 

Sa’adda na ɗan tasa, ina cikin ƙuruciyata

Banda aikin komai, kullum sai ragaita

In ka so kira ni da gwarzo, don na zamo fagen sangarta. 

02.

Da ace ana yin sarki, da na zamo fagen kangarta

Babu moriya a gare ni, balle ma na je makaranta 

Kullum ina kan titi, daga ni sai shiririta 

Bani shakkar kowa, ko Uba ko Ummita. 

03.

Bani tsoron komai, in ka taɓo ni ban lamunta 

Rigima za fa mu yi ta, da ka taɓo ko rigata 

Idan ɓarna aka yi, ka jiyo ana ta biɗa ta 

Rigima sabona, na riga na gawurta. 

04.

Da ka ji ɗaukar magana, ka jiyo ana zance na 

Da ka ji an yo sata, ka jiyo ana nema na

Da ka ji hayya-hayya, ka jiyo ana ta kira na 

Da ka ji an yo zalunci, ka jiyo ana ta kira na. 

05.

Ofishin doka in ka je, can ma akwai sunana 

Cikin jaridu nan ma, duba ka gano hotona 

Ko da fa layi na biyo, ka gano ana zunɗe na

Ni ko fa ban jin komai, ko kaɗan ma a jikina. 

06.

Bani girmama kowa, bani so a yi min raini 

Yanzu ka zama gawa, in dai ka yi min raini 

Ko ka koma gurgu, in na ganka ka kalle ni

Mutanen gari dukka, kowa ya riga ya san ni. 

07.

Ko da Uwata ma, ta san bani son raini 

Hatta Uba guna, yasan bani son raini 

Yanzu za fa a dare, da zarar nai gurnani 

Na zamo hankaka, babu wanda zai kama ni. 

08.

Bani tausayin ɗan kowa, sai ka ce banda imani 

Iyayena suna kuka, na zame musu ɗan kuka 

Bani ma jin komai, don na sa su yin kuka 

Gashi na dame su, kuma gashi na wuce duka. 

09.

Tura da ta kai bango, suka tsine mini albarka 

Nan na gane kurena, na ma gaza yin kuka 

Ciwon daji ya kama ni, na koma kamar nai hauka 

Na je wurin Ummina, ina ta yi mata kuka. 

10.

Na sha baƙar wahala, sai ka ce Ɗanwake 

Hannuna ya girma, ya zamo makeke 

Ina ji ina gani, dole za fa a yanke 

Amma a loton nan, na ma fi so fa a yanke. 

11.

Domin da an yanke, wahalar za fa ta yanke 

Rayuwa ta sa, cutar zuciya ta warke 

Ya Rabbi sarkina, ka yafe ni laifina 

Ya ke Ummina, ki yafe ni laifina. 

12.

Ya kai Abbana, ka yafe ni laifina 

Ya ‘yan uwa guna, ku yafe ni laifina 

Ina makwaftana, ku yafe ni laifina 

Jama’ar garina, ku yafe ni laifina. 

13.

A da na yo ƙwari, sai ka ce ɗan kwakwa 

Yanzu ko sai ladabi, kamar ɗan kaza a gaban kwakwa 

Na ɗauki alƙawari, bani ba ƙarawa 

Allahu shirye ni, daga nan har mutuwa. 

14.

Jamilu dai ɗin ne, ko ku ce Haimana

Ke godiya gun sarki, jalla mahaliccina

A yau ranar Lahadi, sha tara ga wata na

Ashirin da biyun, dubu biyun zamanina.

Amshi:

Wane irin ɗa ne ni?

Wane irin ɗa ne ni?

Wane irin ɗa ne ni?

Gashi yau na canza. 

Bookmark
ClosePlease login

No account yet? Register

Rate the story.

Average: 5 / 5. Rating: 1

As you found it interesting...

Follow us to see more!

<< Tambaya 9Tambaya 11 >>

Drop a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You cannot copy content of this page.
3
Free daily stories remaining!
×