Skip to content
Part 28 of 30 in the Series Tambaya by Haiman Raees

Wata Rana

01.

Da sunanKa Rabbu Azizu

Wanda yai dare yayi rana 

Subhana Jalla Jalalu 

Mai yi wa kowa komai 

Allah Ka ninka salati 

A wurinsa Baban Fati 

Alihi haɗa da sahabu

Da ulama’u gaba ɗaya. 

02.

Wata rana zan yi bayani 

Ba don ina da sani ba 

Wata rana zan zama ba ni 

Ba don ina da nufi ba 

Wata rana za ku guje ni 

Ba don na yi laifi ba 

Wata rana za ku tambaye ni 

Kuma ba zan iya amsawa ba. 

03.

Wata rana za ku tunani 

Ba domin kewa ba 

Wata rana ku so ku ganni 

Ba don ba hoto ba 

Wata rana za ku soni 

Ba tare da na nema ba 

Wata rana za ku yabe ni 

Ba don ganin ido ba. 

04. 

Wata rana tana ga Allah 

Ko wai ba haka ne ba 

Ku zamo kula da sallah 

Wata rana za ku ci riba 

Wata rana za ku ji daɗi 

Ko da maƙiya basu so ba 

Watarana za ku yi nasara 

Ko da ace ba za na gani ba. 

05.

Duniya tana da daɗi 

Ba sai kana da kuɗi ba 

Duniya tana da azaba 

Ba don talauci ɗai ba 

Rayuwa makaranta ce 

Ba sai ga ɗalibi ba 

Tambaya ita kau sila ce 

Ba sai ga wanda ya yo ba. 

06.

Kalmar so na da tasiri

Ba sai ga mai yin so ba

Ƙauna tana da sihiri

Ba sai ga mai tsafi ba

Rayuwa tana da sirri

Ba sai ga mai laifi ba

Mutuwa ƙarshen darasi

Babu wanda ba zata hau ba.

07.

In ka so ka zamo na kirki

Ba wanda ba zai so ba

In ka so ka zamo na banza

Ba wanda za ya yabe ka

In kin zamo ta kirki

Ba wanda ba zai zo ba

In kuma kin zamo ta banza

To nagarin ko ba zai zo ba.

08.

Allahu muna roƙonKa

Ka yafe zunubanmu

Mun yi tuba a gareka

Ka shafe laifukanmu

Albarkacin Baban Fati

Manzo Muhammadu namu

Wanda duk bai ƙaunarsa

Tabbas ya zama garwa. 

Bookmark
ClosePlease login

No account yet? Register

Rate the story.

Average: 5 / 5. Rating: 1

As you found it interesting...

Follow us to see more!

<< Tambaya 27Tambaya 29 >>

Drop a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You cannot copy content of this page.
3
Free daily stories remaining!
×