Bayan fitarsa Iya ta dubi Mami tace” wallahi har yaban tausayi , ‘yarsa ce taja masa komi bamu ba dai”Mami tayi murmushi tace” kuma kin san ance kowa rabonsa zai samu daman” tace” eh hakane ga kuma waccan wutar bata karaso ba , duk da naji kince Safna tace kasar ce ba lafiya ko ?” Mami tace”eh ai Iya kafin suzo ma inshaAllah Widad ta tare a gidanta “ tace” to Allah ya amince” Mami ta ansa da amin.
Basu bude komai dai Uncle dr. ya kawo ba sai dare , a kuma lokacin ne suka sanar da Widad zuwansa ma, su Safwan. . .