Tana shiga Umar ya shigo niƙi niƙi da kaya wai gashi, da hanzari ta ce maza mayar masa, “Ai ya tafi” Umar ya ce.
Karɓa kawai ta yi ta miƙa ɗaki gami da dawowa dan ci gaba da wankinta. Kairiya da ta shigo ne yass Ummu ta watsa mata harara “Malama baki iya sallama ba.”
“Nafa yi sallama yaya ji ne bakiyi ba,” “Eh ai bazan ji ba tunda na kurmance.”
Komawa Khairiyya ta yi batare da ta ce komai ba tayo sallama, “Assalamu alaikum,” gabaki ɗaya suka amsa sannan ta dubi yayar ta su, “Yaya. . .