Bashir Lema ya koma motarsa fuskarsa na fitar da wani lallausan murmushi da alama kaya ya tsinke mishi a gindin kaba ba zai sha wata wahala ba zai mallaki Ummu Radiyya da yake jin kamar bai taɓa son wata ɗiya mace ba sai yau da ya ganta. Tun da ya ga yaron da ya fito a gidan suka tura shi kiran ta ya tabbatar da jinin Isah ne don tsananin kamar da matashin ke yi da shi, shi ya sa bai yi mata maganar komai ba Isah zai ja mishi gaba
Nombar da ta ba shi ya danna sai. . .