Part ɗin abokan zaman Hajiyar muka fara shiga muka gaishe su sai muka yi ƙarshe da na Hajiyarsu.
Tana ta ina ta saka ina ta aje da ni hakan ya sa ni farin ciki, an kawo mana abinci shi ya ci ni ban ci ba, sai da ya kammala ta dube shi "Su Amal sun iso ko?
Ya ce E. Ta ce " Umar ya ce ya gan ta ɗazu, ban ji daɗin shigar da aka gan ta da ita ba, nan fa Arewa ce cikin hausawa musulmai ba ƙasar waje ba garin arna. Ya'yanka mata ne ka. . .