Ƙunshin hannunta da yake rike cikin na farin matashin saurayin ya fara bi da kallo, ƙirjin shi na zafi kamar zai buɗe, kafin ya ga saurayin ya miƙa kai saitin kunnen Waheedah yana raɗa mata wata magana da ta sa ta yin dariyar nan tata da take kashe mishi jiki. Bai san ya ƙarasa wajen ba saboda wani irin kishi da ya turnuƙe shi har duhu-duhu yake gani, tsakanin su ya shiga yana huci kamar kububuwa.
"Lafiya?"
Saurayin ya faɗa yana kallon Abdulƙadir ɗin kamar ya ga mahaukaci.
"Lafiya kake tambayata? Baka san. . .