Bayan Wata Shida
Ba zata ce ga lokacin da ta taɓa jin daɗin rayuwarta irin watanni ukun nan ba, tana gama iddarta ta fara shiga gari yadda take so, satinta ɗaya bayan rabuwarsu da Abdulƙadir ta samu ta fita da rana ita da Asma suka je gidan suka kwashe kayan kitchen ɗinta, bata samu Abdulƙadir a gidan ba, sai Waheedah da sallamar su kawai ta amsa. Har da kayan abincin da suke kitchen ɗin kaf ta kwashe tana tafiya da su gida. Haka ta ce wa Mama cikin kuɗin kayan kitchen ɗinta ne. . .
Littafin Nan yayi ma’ana sosai Allah ya Kara basira Lubnah
Littafin yayi ma’ana sooosai da sosai, sai kin ga yadda na ke jin Abdulkadir a rai na kaman da gaske in samo shi in masa shegen duka wallahi amma Alhamdulillah everything fell in place. Allah ya kara basira. Mun gode