Tun da aka yi rasuwar har kwana biyu ba ta ga Ahmad ba, shi ya sa ba ta san halin da yake ciki ba. Kuma babu hanyar da za ta samun sanin hakan, saboda ko wane lokaci gidan cike yake da mutane, wadannan su zo, za wadannan su tafi.
Ita kam ma ta kanta take yi, saboda wannan cikin sosai laulayi take yi, ga shi ba ta son hayaniya, ga kuma jimamin mutuwa.
Saboda Galidima uba ta dauke shi, duk da Sai ta yi zuwa sama biyar gidan basu hadu ba, time da za ta zo yana fada, time da. . .