Da wannan tunanin ya kammala alwalar ya shige ɗaki ya tada kabbarar sallah, sallar ma ba da cikakkiyar nutsuwa ya gabatar da ita ba. Yana nan zaune a inda ya idar da sallar Larai ta farka daga bacci tana miƙa daga zaunen da ta yi a kan gadon, ba hamdala ba salati bare kuma gaida miji, ta fara kwala kiran Al'mustapha.
Malam Jibrin ya kalle ta ya girgiza kai tare da faɗin, "Ya tafi makaranta."
Cike da hargagi kuwa ta fara masifa, "Kai wane irin mutum ne? Ya za ka bar shi ya tafi bayan ka san. . .
Ahh I was immersed in the book kawai na ga ba continuation😩. Dan Allah a karasa mana littafin