Wani kallo ya watsa mata ya ja tsaki ya ce, "Ki je ki tambayi uwarki ita ce take da cikakkiyar amsar tambayarki." Ya bankaɗa labule ya shige ya bar ta a tsaye. Nishi kawai Asabe take yi tana faɗin wayyo hannunta. Waya ƴarta ta biyu mai suna Fadeela ta ɗauko ta kira wani Kawunsu a kan ya zo ya taimaka su kai mahaifiyarsu asibiti.
Faɗa ya hau yi mata ya ce shi ba ruwansa ya fita daga sabgarsu duk tsuntsun da ya ja ruwa shi ruwa yake duka. Da taimakon wani saurayinta wanda suke sheƙe ayarsu. . .