Su uku suka nufo ta da sauri ta juya tana fadin
"Don Allah ku duba min nan kamar naga jijiyar wuyan tana motsawa.
Ta fada a rikice tana tab'a wurin a wuyan Abdulhameed.
Daya daga cikin masu tsaron kofar ya fada a ranshi cewa matar nan fa tana dab da ta haukace sai kace akan danta aka soma mutuwa kullum tana kwakwufe da gawa kenan tana son nuna mana danta bai mutu ba kenan? duk mutanen da suka rasa ahalin su uwa ko uba ko dangi duk basu san kaddara ba kenan sai ita?
Yana tsaye yana mita. . .