"Allazee wahidun Allah da girma yake ! Kalmar ta shiga kunnen Kaisar da yake kwance a saman shimfidar wacce ya dawo ya iske bayan tsohon ya maido shi daga masallacin da ya kaishi wanda bai san ko a wacce shiyyar bane
Ya tashi zaune inda ya hango tsohon rike da fitilar sa mai shegen haske.
"yi hakuri dan samari na tayar da kai daga bacci ko?.
"A a baba ba bacci nake ba.
cewar Kaisar
"Har nayi nisa naji suna maganar kashe ka a gobe shine na dawo don alheri ne ya hada mu da Kai ba mugunta ba kuma. . .