"Kai dai ayi sha ani uban gida na amma wannan yarinyar ba kuruciya bace akan ta sai dai wulakanci abu kad'an fa zata ce ma mutum matsiyaci gori a wurin ta tamkar a kanta aka saukar dashi zagi da mari ko Kai ka yankewa k'asa cibiya bata jin wahalar yi maka ko kai din sau nawa tana maka? na dai kula kamar kana son ta ne don kallon ka ma kadai gare ta ya nuna hakan.
Kaisar yayi murmushi yana shafa kyakkyawwr sumar kanshi wacce ta kara fidda mishi sirrin kyawun sa ya dubi malam Ango yana fadin. . .