"Abdulhameed, mutum kamata ya dace da karya ko magana biyu? Yaya za ka kalle ni idan na yi maka alkawarin karya sai kazo sai kaji an daura auren Nadiya da wani ba kai ba? tsohon banza ko kuwa makaryaci mayaudari? to ko kusa ko alama kar ka saka ran auren Nadiya don babu hadi kazo a makare.
"Ka tausayawa halin da zan shiga daddy don Allah kar kayi min haka Daddy.
"Abdulhameed be a man Kaji? Idan so ya zama cuta to hakuri ne maganin wannan cutar da ace kazo tun kafin yau da na yi maka alfarmar da ka. . .