"Daddy ni fa duka ma ban fahimci komai a cikin maganar nan ba sai ta cikin da ka fada. wai ciki na Nadiya take dauke da shi Daddy? Allah na gode maka Daddy kuma shine zaka hana ni auren ta Daddy? nine ai nafi cancantar na zama miijn ta tunda ga dan mu ma zai iso duniya.
Alhaji Iro ya dubi Abdulhameed yana fadin
Baka fahimci abinda nake nufi ba kenan abdulhameed? to daina Kiran cikin Nadiya naka don babu hadi ka san hakan don da da hadi da an sanar muku don haka kar ka kuma zuwa gidan nan. . .