Kuka take tamkar ranta zai fita, ga wani gumi daya wanke mata fuska duk sanyin da ke gauraye ɗakin.
"Wallahi ko ki fiddoman ɗiyata ko kuma kiyi ta bakin aurenki, kinji na faɗa maki, ace yau tsawon wata hudu kenan kinturata biki ashe bama bikin danginku bane can biƙin ƙawar dana hanata zuwane, tsabar kin ɗaukeni banda mutumci a wurinki shine kikayi mani ƙarya,to kinji na rantse maki indai ɗiyara ta ƙara kwana goma bata dawoba kema saidai kitafi gidanku."Alhaji AbdallahYa ƙarashe maganar yayi waje ranshi a matuƙar 6ace.
Cikin muryar daga jinta kasan tasha. . .