Basarake ya dinga rarrashinta da daddad'an magana har ya samu ta yi shiru, sannan ya samu damar gaisawa da Ummi. A cikin farin cikin ganin juna suka baje a nan falon yana cin abinci suna fira har ya k'are, sannan Kakale ta fara magana tana cewa,
"Wai kai ba ka ga na fara tsufa ba? A ce shekara biyar kana zaune babu mata, ka fa yi wa kanka fad'a ALIYU, don ALLAH ma ai sai ya yi maka hisabi da gangar jikinka. Saboda ALLAH kai fa ba saurayi ba ne amma a ce har yanzu ka kasa. . .
Masha Allah
Very good
Very good
Very interesting book
I will like to read the book