Ni ma na bita. Tana mamutse da ita suka shiga ɗakin, murna yaya Azima take sosai.Ita kuma ta faɗa kan Innarmu tana kuka. Mutanen gidan ma kan ka ce me, sun cika ɗakin.
Sai da aka natsa kowa ya kama gabansa sai mu kaɗai. Labari ake ta bata na bayan bata,zuwa can sai ta zura min ido, "Wai Shuhainar Inna ce ta zama haka?"Jawo ni ta yi, "Ba ki gane ni ba ko?
Na ce, "Da dai a hanya na haɗu da ke zan rinƙa tunanin ina na san ki, dan ko hotunanki. . .