Sosai maganar Umman Abbas ta saka Aunty cikin rudani, dan kuwa alamu sun nuna cikin tsananin fushi take, "Wata sabuwa kuma", Aunty ta fada cike da jimami, lokaci daya kuma ta sauke nannauyar ajiyar zuciya, Asma'u da gabanta ke dukan uku-uku ta ce "Aunty me ta ce maki?", sai da Aunty ta nisa kana ta ce "Wai Abbas ne a Asibiti", tsabar firgici Asma'u bata san lokacin da ta dafe kirji tare da fadin "Asiti! Me ya same shi?", don kuwa ta san duk abin da ya faru da shi ita ce sila, "Ta ya zan san. . .