Miraran su Aunty suka ga tsabar raunin zuciyar Abbas, dangane da son da yake ma Asma'u, har suka yi tsammanin haƙarsu zata cimma ruwa, cike da zaƙuwa Aunty ta katse mashi tunani ta hanyar faɗin "Ka yi shiru Abbas."
Murmushin da iyakar sa kumci ya yi, lokaci ɗaya kuma ya dube ta cikin sigar tausayin kansa, muryarsa na karkarwa ya ce "Ku gafarce ni Aunty bisa ga hukuncin da na san ba zai yi maku daɗi ba", Sosai wannan magana ta Abbas ta ƙara saurin bugun zukatan da ke ɗakin, duk da ba su ji. . .