Sai bayan sallar isha'i adaidaita ta sauke Nu'aymah a kan layinsu ta gangaro zuwa gidanta da ƙafa. A kulle ta tarar da gidan, da mamaki take kallon kwaɗon da ke sarƙafe a ƙofar tare da buɗe jakar hannunta ta ciro mabuɗi a ranta tana mamakin yaushe Salis ya ari ƙafar shanshani, ita dai a iya sanin ta da shi a masallacin layinsu yake sallar isha, ranar da ba ya jin bin jam'i ma a gida yake yi. Kuma daga ya shigo shi kenan ba ya sake fita in dai ba wani uzuri ne. . .