Ga Fadime ko tunda ta shiga cikin gidan take tsaye rungume da Abbati har yanzu ta gagara zuba masa ruwan da aka faɗa mata. Suma ne, barci ne, a'ah mutuwa ya yi, masani kam sai Allah. Ta yi tsaye tana jiran ta ga ta inda wanda ke amsa sunan mijin nata zai farmata, amman shiru kake ji ba ko motsinsa balle ta sa ran zai shigo gidan. Hakan bai sa ta gaji da tsayuwar ba har gurin ƙarfe goma na dare da ya shigo.
To shima turus ya yi ganinta tsaye , sai kuma ya kaɗa kai. . .