Kwana Biyu Da Suka Gabata
"Surukin naki ne da na yi alƙawarin kawo miki a duk sa'adda na koma. Gashi nan ya zo gare ki yau, zai kuma dawwama a gurinki har mu ga abinda gobe za ta haifar."
Kallon rashin fahimta ta masa tana kallon ɗan matashin yaron.
"Yanzu wannan jikan Falmata ne? Allah mai iko, ka ga fa babu ta inda ya kwaso dangi."
"Ikon Allah kenan. Idan kika ga Babansa kuma ance ko yatsansa bai bari ba..."
"Bai jin kwari Umma a masa wanka, ga magungunansa ya sha. Wannan yaron ɗan amana ne. . .