Skip to content
Part 30 of 30 in the Series Falsafa by Haiman Raees

Falsafa

Na fara da sunan Rabbana

Allahu Kai ne ɗaya sarkina

Kai ka zaɓa mini komaina

Na gode wa Ilahu maƙagina.

Yabo da yawan dubunnai

Ga Habibu kawai mu yi mai

Manzonmu da Sarki yai mai

Dukkan ni’ima da maimai.

Ga falsafa da bakinta

Tana ta yaɗa muradanta

Cikin kasuwa, makaranta

Fatan kowa yana jinta.

Falsafa ilimi ne faffaɗa

Rijiyar in har kaf faɗa

A wurin ilimi ka zama ɗa

Ka haure duk tirgaɗa.

Ko Baba ma yana da Baba

Uban wani ba na wani ba

Ɗan mutum ya fi na dabba

Ba a samu mai tantama ba.

Ɓarawo shi ya san lunguna

Ɗan daba shi ya san adduna

Mata ne sirrin adana

Taguwa sarauniyar riguna.

Mata ne ni’imar duniya

Kuma su ne rigimar duniya

Soyayya daɗin zuciya

Nasarar rayuwa ƙarfin zuciya.

Cin hakin sama sai dai raƙumi

Makaho ko me dundumi

Ba ya wasa da kandami

Ɗanɗanon ya yi fa galmi.

Lulluɓi darajar mata 

Zubar jini ai sai kwata 

Mugun sarki ke mugunta 

Baƙin kishi sai mata. 

Zantukan kurman baituka

Baitukan ɓoyon zantuka

Haushi ku sani sai karnuka

Haiman ke jawo baituka. 

<< Falsafa 29

Drop a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You cannot copy content of this page.
2
Free daily stories remaining!
×