‘Amna, wato a rayuwa kowa da kika gani da irin jarrabawar da Allah ke mai saboda haka ina so ki cigaba da addu’a kuma ki bar ma Allah zabi inshaAllahu zaki ga sakamako na alkairi kuma zaki ci ribar biyayya.” Kalaman ammi na kenan lokacin da abbu yayi maganan aure na.Madalla da uwa ta gari,Alhamdulillah.
*****
Lallai ammi kinyi gaskiya tabbas a rayuwa komai ya zo mai wucewa ne haka nan duk rintsi in kayi haquri kayi biyayya zaka ci riba da izinin Allah, a matsayin da nake a yau ina kara gode ma Allah.
*****
'Ammi’ na kira. . .