Likitan ya yi baya a tsorace ya ji ya daki wani abu kamar dutse, ya waiga da sauri ya ga wannan ƙaton ne ya sanya ƙirjinsa ya tokare shi yana kallonsa cike da gargaɗi, ya sauke numfashi da ƙyar yana haɗe hannayensa guri guda alamun bai sake taɓata, cikin rawar murya ya ce,
"yallaɓai ina rantse maka da Allah na taɓa yarinyar nan da niyyar kwaƙule cikin nan za ta iya mutuwa. Bansan yadda zan yi aikin nan ba tare da na illata ta ba, ka taimake ni ka rabani da aikin nan na. . .