Karshen Tuka-Tuki
Koda ta hau saman wayarta ta lalubo ta latsa lambobinsa da kullum sune na farko a layin da kira ke shigowa. Rinni biyu ta ji ya ɗaga.
“Ka yi hakuri, domin Allah..”
Kalmomin suka fita tamkar an fisgo su.
A can ɓangarensa runtse idanuwansa ya yi da ƙarfi yana tasbihi ga ubangijin talikai a sa’ilin da sautin muryarta ya shiga cikin kunnuwansa. Sai ya ji sak Hamdiyya a wani dare da take furta irin wannan kalmomin gare shi. “_Ka yi haƙuri, domin Allah Huzaif kar ka ce baka taɓa so na ba. . .
Rubutu kwarai ya wa’azan tar damu ya Kuma samu nishadi, Allah Ya cigaba da zama jagoran ki. Amin