Bitar Al-ƙur'ani muka yi bayan mun idar da sallar asba, muka koma bacci, sai bakwai na safe na farka.
"Ya Salam!" Na faɗa bayan na duba agogon bangon ɗakin, na tashi zaune, hulata na saka, na miƙe tsaye tare da kiran sunan Fatima, Juyi ta yi ta ce,
"Na'am Yaya."
Na ce mata "Ku tashi mun makara yau har bakwai ta yi." Ina maganar ina buɗe window, hazo ne ma ya lulluɓe sararin samaniya.
Na juya kan Nana da ke ta juyi kan katifa na miƙar da ita tsaye ina faɗin. . .