Skip to content
Part 44 of 59 in the Series Halin Rayuwa by Hafsat C. Sodangi

Na dai san kawai ba karamin farin ciki nayi ba, saboda ganin da nayi nima zan samu kani ko kanwa, in musu nima irin abinda Yaya Dijah take yi min na kulawa da tausayawa.

Muna cikin wannan halin sai ga Baba Lantana tana shigowa da kayanta kwararam-kwararam tana ajiye su a tsakar gida, tana komawa tana shigowa da wasu. Ta rame tayi baki tanfar wacce ta tashi daga jinya mai tsanani.

Yaya haka kuma naga an shigar min daki? Wannan wane irin neman magana ne? ba sakina aka yi ba, ba komai ba sai kuma kawai daga na fita da kayana ayi maza a shige nin daki? Ke Yachuwuna kina ganin irin wannan neman maganan ko?

Nayi maza na kalleta a firgice na soma gaisheta cikin wani irin yanayi saboda rashin sabo da yin magana da ita.

Babana ya fito daga dakin Safara ya wuce zai fita bai kulata ba ta bishi da kallo, Mallam kana gani na dawo ba za ka kula ni ba? shiru yayi yana tafiyarshi, tayi maza ta sake ce mishi to kayi mata magana ta fita daga dakina ta bani wuri in sa kayana don kar hakan ya zama wata fitina a tsakaninmu.

Bai tanka ba yayi ficewarshi ya tafi, bakin ciki ya kama ta ta ce “Wannan shiru na Mallam, wannan shiru na Mallam ashe ba zai daina ba?” Ta jinjina kai ta rasa abinda zata ce. A zuciyata na ce, da dai kin san abinda zai faru kenan da ba ki yi mishi abinda ki ka yi mishin ba.

Baba Lantana taja ta tsaya cikin wani irin yanayi na rashin sanin abin yi, da dai ba su taba gwada yar kashi da Safara ba, da tayi wani yunkuri. To babu hali, tana shakka gashi kuma Safara sai kai kawo take yi ko Kallon inda take kuma bata yi ba, balle ta tanka mata.

Ta gaji da tsayuwa tayi kamar ta kwashe kayan nata ta koma inda ta fito, ban san kuma me ta tuna ba. Sai naga ta bude wancan dakin tasa kayan nata a ciki. Ta gyara tayi zamanta.

Tsoro yayi matukar kama ni, ko me yasa Baba Lantana tayi irin wannan canzawar? Mace ce mai fadin rai, nuna isa da ganin kowa ma bai isa ba, wani abu taje ta gano ya sa ta tayi wannan canzawar ko kuwa dai wani abin take shiryawa?

Na gama abincin daren da nayi don tun zuwan Anti Safara mafi yawancin girkinta ni take sawa in yi, to balle kuma yanzu da take fama da laulayin cikinta.

Ina gamawa na zubawa kowa har da Baba Lantanan na kai mata nata na yiwa Babana shimfidar tabarma a tsakar gida inda ya saba zama, na ajiye mishi nashi a nan.

Yana dawowa daga Masallaci ya shiga wurin Anti Safara yayi mata sannu da jiki, ya dawo ya hau kan tabarmarshi ya zauna ya soma cin abincinshi.

Baba Lantana ta fito tazo daga bakin kofarta tana yi mishi magana, bai ce mata komai ba. To ka shiga daga ciki mana Mallam, wannan hirar da ka ke yi a waje ai ya wuce ka’ida.”

Bai ce mata kala bá, har bacci ya dauke ni suna nan a wurin shi yana kan tabarma a zaune, ya jingina da jikin bango, ita kuma tana daga bakin kofarta.

Ban san yadda aka yi ba, cikin dare ne kawai na farka a dalilin buga min kofar dakina da take yi da iyakacin karfinta tana gaya min wai in fito in ga abinda Babana yake yi, girkinta ne amma gashi nan ya sake ta ya shige dakin wannan tsinanniyar matar yana yin abinda babu kyau.

Duk da katse min baccin  da tayi ta kuma hana ni sake runtsawa saboda buga min kofar da taki dainawa ban motsa ba, balle in yi yunkurin saukówa daga gadon nawa in fito.

Ban sani ba ko ta gane ba zan fito ba ne yasa ta bar tawa kofar ta koma buga tasu, a zuciyata na ce dama tuntuni hakan kika yi da yafi miki.

Girki nane fa Mallam, yau a wurina fa kake, nan take ta soma kuka tana fadin “Ban yafe maka ba Mallam.  Bazan yafe maka satan kwanan da kayi min kaje wurinta ba.

Ban taba ji ko ganin Baba Lantana tana kuka ba a zaman da nayi da ita ba sai rannan,  kuka kuma bana wasa ba, ko da yake babu wata kyakkyawar alaka ko wata kauna sa ke tsakanina da Baba Lantana. 

Amma kuma hakan bai sa naji dadin yanda Baban nawa yayi ba duk da dai itama bata taba yiwa wani adalci ba,  a lokacin da ta samu damarta.

Gari na wayewa nayi maza na gama abinda zan yi na suri jakata na saba a kafada na fita gidan na bar Baba Lantana a tsakar gida a tsaye rike da shirgegiyar tabarya a hannunta, tana rantsuwar sai dai in ba za su fito ba, amma sai ta rafke su da tabaryar hannun nata. Na wuce na tati makarantar da nake zuwa TP, wato (Teaching Practice) saboda gab nake da kamala karatuna a Makarantar addini mai zurfi.

A hanyata ta dawowa gida zuciyata tunani take yi kan yadda ta kare tsakanin Baba Lantana da su Babana.

Ina isa gida ban san yadda aka yi ba sai kuma naga Baba Lantana da na bari da tabarya a hannu da kulu a goshi, ban tambayi Safara yadda aka yi ba, to balle kuma Baba Lantana da ban ma iya yin wata magana da ita ba.

“Kin dawo ne?” Na ce mata “Eh.” “To ga fura nan da nama Babanki ya aiko da shi, na diban miki, nace to sannu. A zuciyata nace ko ba komai dai yanzu ina da kaso a abinda Babana yake kawowa.

Na gama cin naman ina shan furar sai ga Baba Lantana ta fado cikin dakin nawa, nayi maza na mike tsaye saboda tsoratar da nayi, tunda ban taba ganin ta shigo dakin nawa ba.

Ban sani ba ko itama ta gane tsoratar da nayi ne yasa ta fara yi min bayanin abinda ya kawo tan cikin sauri kinga kulun goshin nan nawa ko?”

Na daga ido na kalli kulun goshin nata da take tabawa da hannunta, kan in ce mata na gani sai kawai naji ta ce min, To Mallam ne yayi min shi.

Nayi maza na sake kallon kulun saboda razanar da nayi da jin bayanin nata, kulun ya amsa sunan kulun ban san yadda aka yi ba naji bakina ya ce mata sannu, tayi maza ta ce yauwa.

A tsakanin wannan lokacin ba sai an gaya min ba, ni da kaina nasan Baba Lantana tana cikin wani halin ba, tsananin bacin rai kowane lokaci a cikin kuka take.

Ashe haka Mallam yake? Tafdijam! Ashe shiru-shirun nan na shi ba na kalau ba ne? Dama fa nasha jin ana cewa ka ji tsoron mai shiru-shiru, ban taba yarda ba sai a wannan lokacin, yanzu ne na gane lalle Mallam munafuki ne.

Ko kadan bana jin tausayin Baba Lantana, saboda azabtarwar da tayi mana ni da Babana, ta wulakantamu ta tozarta mu, gara ma ni komai tayi min da sauki tunda a kuruciyata tayi min, amma shi Babana ta same shi ne da girmanshi da mutuncin shi a tsakanin mutanen unguwa.

Kowa yana girmama shi saboda ya kame kanshi bai shiga harkar kowa, bai sa ido kan abinda wani yake yi, balle ya yi gaba ya bada labari.

Bai sa ido kan abin wani ya gamsu da abinda yake da shi amma zuwan Baba Lantana gidanmu sai da ta maida shi abin kwatancen mutane.

Komai aka yi sai ka ji sun ce kai haba, kar ka maida mu Mallam Habu mai tumatir Mana, to amma duk da haka ba na jin dadin ganin yanda yake yi na hanata kwananta da yake yi yana barinta tana kwana ihu tunda a karatun da ake yi mana Malamai suna yin bayani kan rabon kwana a tsakanin mata wajibi ne abinda kayi a can ne bai zamo lalle sai kayi shi a nan ba.

Amma a kaiwa mace kwanan wannen dole ne, to shi Babana baya kaiwa. Da dai ace ina cikin masu baiwa Babana shawara, to da nace mishi cikin biyu ya zabi daya ya yi, ko dai ya rinka shiga dakin Baba Lantana yana kwana tunda dai zaman aurenshi take yi ko kuma ya ce mata ta tafi ya sake ta don ya sauwakewa kanshi al’amura.

Sanin da nayi hakan da ake yi bai yi ba, ya sa ni tafiya gidan Yaya Dijah nayi mata bayani, a yatsine ta kalle ni to ke ina ruwanki? Inta ji babu dadi ta tafi mana.

Na ce, A’a Yaya Dijah, ai ba don ita nake maganar ba, nayi mata gwargwadon bayanin da zan yi mata, ta ce to naji in na zo gidan zan yi magana da ma ina so in zo wurin Baban na ce mata ko na kama hanya na dawo gida.

Yaya Dijah ba ta zo gida ba sai a ranar Laraba da safe, muna zaune a falon Anti Safara inda nan ne wurin zaman Babana a kowane lokaci.

Hira muke yi cikin yanayi na jin dadi ni da shi da Yaya Dijah, yayin da Anti Safara ke kicin tana shirya abincin rana, ita kuwa Baba Lantana da yanzu ko tsakar gida bata cika fitowa ba take dakinta.

“Oh Baba, yanzu har a irin alherin nan da yake shirin samunmu na Mero ma zata samu kani a bayanta zamu sake samun dan uwa ke ‘yar uwa, maimakon mu biyu ko mu koma mu uku ba za ka yi hakuri ka gaya mana inda danginka suke ba?

Ba don mu kadai ba Baba ba ma don mu ba tunda mu kam ni da Mairo ai mun riga mun mallaki hankulanmu, mun fuskanci rayuwa mun kuma fara gane yanda take ba, komai dan Adam yake so yake samu ba.

Don wadannan da za su zo daga baya Baba gaya mana inda danginka da garinmu yake in wani laifi suka yi maka ni Hadiza yarka na roke ka ka yafe musu to ko menene? Ai ya wuce Baba kayi hakuri ka…

Tayi maza tayi dib taja bakinta tayi shiru ta bar karasa maganar watakila sai lokacinne ta daga ido ta kalli yanayin da ke fuskarshi wanda ni tunda ta fara maganar  na gani shi yasa nayi ta taba ta bata gane abinda nake nufi ba.

Ta tashi ta bar dakin saboda daurewar fuskar tashi, takai matuka nima na tashi na biyo ta muka dawo dakina muka zauna tayi kuka har a gaji ta share hawayenta.

Kwana biyu bayan nan Anti Safara take ba ni labarin cewar Babana ba lafiya ta da shi ba, karfin hali ne kawai yake yi yasa ake ganinshi yana yawo.

Na ce, To. A zuciyata dai fatana da addu’ata bai wuce ya zamo ba maganar da Yaya Dijah tayi mishi ba ne yake nema ya tayar mishi da jikin.

Na rasa yanda zaa yi in fuskance shi da maganar rashin lafiyar tashi, saboda tun daga ranar da na raka Yaya Dijah tayi mishi wannan maganar fuskarshi daure take.

A zuciyata na kudurawa kaina ba zan sake yarda Yaya Dijah ta ce min za ta yi mishi irin wanan maganar in bar ta ba, tunda baya so, shi kenan a kyale shi, yan uwanshi ne, shi yasan abinda ke tsakaninsu.

Abunda ya fi komai muhimmanci wurin da uba ne, tunda shi ne asali to mun gode tunda muna da shi kowa yasan muna da shi mun kuma san shi, mun rayu tare da shi, babu wanda zai yi mana gorin rashin uba, sai na rashin ‘yan uwan uba. Wasu suna nan su ba su ma san ubannin nasu ba balle suyi maganar danginshi suna nan kila a dadin su ma kuma suna rayuwarsu don haka na hakura itama zan gaya mata ta hakura suma yan bayan in sun hakuran kamar yanda suka same mu mu ma akan hakurin.

Rannan da daddare Anti Safara ta buga min kofa gabana yayi mummunan yankewa don kuwa na tabbatar jikin Babana ne yayi tsanani yasa aka tashe ni tunda tunda rana ina kallon irin wahalar da yake yi akan kai kawon numfashinshi da bai karasawa ya sauka cikn ciki sai dai a Kirji.

Babu yanda Yaya Dijah da naje na kirawo a dalilin jikin nashi bata yi da shi ba akan muje asibiti ya ki yarda.

Da sauri na balle kofar na fito na nufi dakin Anti Safara da ke bude a kasa, na samu Babana na zaune a cikin yanayin rauni mai yawa.

Ko zama da kyau bai iyawa saboda ya riga ya rasa karfi a tare da shi, numfashi sai kaiwa da kawowa yake yi a tsakanin kirjinshi da makogoron shi. “Sannu Mallam, Ubangiji ya baka lafiya.” Tana sannun tana share mishi hawayen da ke diga daga goshin shi, tana kuma kuka.

Jikina ya dauki bari saboda yadda al’amarin ya tuna min da yadda naga Innata a daren da zata bar duniya. Da gudu na juya na bude kofa na bar gida.

Nufina wai in je gidan Yaya Dijah in kirata tazo ta taya ni ganin abinda Babana yake yi, sai kawai muka yi kicibis da Isiyaku.

Ban san daga ina yake ba a wannan tsohon daren ina za ki haka Anti? Me ya same ki ki ke kuka haka? Ban iya ba shi amsa ba jikin Baba ne ya tashi?  Nayi maza nace mishi “Eh”  To ina zaki yanzu sha biyu saura kwata ne fa na dare.

In asibiti kike so a kai shi ga makwabta.” Lokacin ne na tuna ashe ma Baba Baidu ya kamata in fara gayawa ba wani ba, balle Yaya Dijah da ba ma kusa muke ba, tunda ance makwabcinka na kusa shi ne mutum na farko da ya kamata ya taimake ka, in har ka shiga halin bukatar taimako.

Tare da shi muka je na fara buga kofar gidan Baba Baidu, sai da ya ji ya bude kofar dakinshi zai fito sannan ya ce min,  Bari in nemo mana motar da za ta kai mu.

Na ce mishi “To, Isyaku na gode.” Tamfar dai ba shi ne Isiyaku da na share ba ko amsa gaisuwarshi ba.

Ina tsaye a tsakar gida bayan na shiga dakina nayi shiru na debo duk kudin da nake da su, kuka mai yawa nake yi saboda yanda nake jin Babana yana magana cikin jarumtaka da kyar da kyar.

Amanata yake baiwa Baba Baidu da matarshi, ni Mero sa shiga uku zan rasa uba mahaifi kamar yanda na rasa mehaifiyata yau ya ya zan yi?

Gare ka nake bauta Allah, gare ka nake neman taimako ya Ubangiji, abinda kawai nake ta nanatawa kenan. Ana cikin hakan naji zuciyata tana zargina da cewar ni da Yaya Dijah muka fara haddasa mishi ciwon nashi da muka tasa shi a gaba muka yi mishi maganar da baya so.

<< Halin Rayuwa 43Halin Rayuwa 45 >>

Drop a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You cannot copy content of this page.
2
Free daily stories remaining!
×