Nayi maza na ce mata gashi nan saboda taimakon nata yazo min ne a daidai lokacin da nake bukatarshi.
Duk da taimakon da Jumare ta kawo min da aiken da Babah Sumaye tayi-tayi na ayi kaza kar ayi kaza abincin da muka girkan yawanshi ba kadan ba ne, dandanonshi kuma ba wani mai gamsarwa ba ne ko in da aiken nata da zuwan Jumaren wane irin kwaba zan yi? Oho.
Duk da min karbi girkin abincinmu Babana bai daina bada kayan miya a gidan Baba Hodijo ba babu kuma wani abinda ya canza a tsakani ni kam ma dai. . .