Muna shiga gida ta takarkare ta sakar min wani irin azababben dundu da yayi sanadin da na durkusa a kasa nan take kuma ta rufe ni da duka tana kuma yi min tambayoyi ni na kashe miki uwarki ne da za ki tasa ni a gaba da masifa? Kiyi min sata kar in yi magana? Ni nan da ki ke kallona ubanki ma ba tsoro yake bani ba balle wasu can banza a banza in na gama dukan naki kije yau ma ki nuna musu ina nan ina jiransu su zo Su same ni don ni nan da ki ke. . .