Namsiyya tana isa gida ta samu mahaifiyar ta tana jefa ɗanwake acikin tukunya saman murhu, sai ƙanwarta na shara wata na wanke - wanke,
“Daga ina kike? ”.
Itace tanbayar da mahaifiyarta tajefa mata tana kafeta da ido
Dam! Dam!! Gaban Namsiyya yayi wani irin mugun bugu don ita tuni ta manta da kayan makarantar ta dake can sabon kawo gidan kakarsu Sholy, sai ta dabar barce ta hau kame kame da tunanin abinda zatace da mama ta yadda da ita, dan danan zufa ta fara karyo mata tarasa abin faɗa.
“ Dake fa nake nace daga ina kike ”
Mama tasake mai mai. . .