Ban san ko sau nawa na yi attempting kiran Bashir ko tura mishi sako a kan lamarin ina gogewa ba.
Karshe dai na ba Uwani kudi na lissafa mata abun da nake so ta siyo min, da zai mana kwana biyu.
Sosai nake mamakin lamarin Sarai, a ina ta san wannan rashin mutunci? Kar dai yar kauyen da nake raina wa ta dora min ciwon zuciya, saboda tun yanzu na fara jin gara min kishi da Maman Khalil sau dubu a kan Sarai. Farawa da iya wa.
Inda Allah Ya taimake ni ina sana'a, kuma cikin ikon Allah. . .