"Wato Khadija ni ban isa ki yi min abin da nake so ba ko? Kin rantse dai sai kin bata min gida ko? Ke ce babba amma kina abu kamar ke ce yarinyar? Kullum kina kirkiro min fitina. Me Nana za ta yi da warin takalmi silifas? Kuma sau nawa ina fada miki ba na son kowa yana shigowa gidana? Wato na fada ya shiga ta nan, ya, kuma fita ta nan (ya yi maganar hade da nuna min kunnuwanshi guda biyu) "
Shiru na yi ko motsi ban yi ba, ya kuma ɗorawa daga dawowa ta ko hutawa ban yi. . .
Kano