A lokacin ne na basu labarin abin da ya faru. Bayan na diga aya Inna ta ce "Ai a bar hali a ci me? Kuma nono guba, daman idan Sarai ba ta yi masifa ba me za ta yi? Na nunawa Bashir illar auran nan ya ce ba haka ba, wai wancan mijin nata yaro ne, shi kuma da hankalinshi zai biye mata ne. To ga shi nan ba aje ko ina ba ta nuna mishi iyakarta, yanzu wannan barnar da ta yi mishi nawa zai kashe ya gyarata, ga yaronshi da ta sanya ya nakasa... "
Yaya Habi ta tare. . .