Shiru na yi hade da nazarin maganganun na shi, yanzu da ba Affan a gidan ji nake kamar ba kowa, ga shi duk mun dokanta da son ganin shi, Sai kuma kawai Bashir din ya dawo mana hannu na dukan cinya.
A hankali na ce "Ta yi hak'uri mana ya dawo mu gan shi, in ya so sai ya koma daga baya"
Ya dan yi shiru kamar ba zai ce komai ba, Sai kuma ya ce "Ko hakan na yi sai in ji kamar na nunawa Rahma iyakarta, ba tun yanzu take kulafuci a kan yaran nan ba, kuma. . .