Ni dai na zuba ido in ga inda alakar nan za ta kai su, idan ma auran juna za su yi maraba da zuwanta, ni dai permanent sit gare Ni, Kuma na daina daga hankalina a kan kishiya, bare yanzu da ba ni kadai ba ce.
Suna isa ya kira ni ya haɗa ni da Zahra, mu ka gaisa cike da fara'ar nan tata ta wayayyun mata. Ta kara sanar min da sha Allah gobe za ta kai Khaleel school Abuja. Cikin tsokana na ce "To amana dai na ba ki, idan kin ga akwai wahala kawai ki. . .