Kara bata rai ya yi kafin ya ce " Thank God ma ba na nan za a yi bikin, kuma ni komai kirkinta babu ruwana da ita" daga haka ya yanke wayar, da alama babu Rahma a wurin na tabbata da sai ta kara kira.
Misalin karfe takwas Bashir ya shigo gidan shi da Khaleel, tun da ya shigo kuma yake tambaya ta ina Maama. Da alama Khaleel ya labarta mishi abin da ta yi. Na ce "Tana dakinsu Khaleel"
Zuwa can sai ga shi sun fito hannunta daya cikin na shi, ɗayan kuma tana share hawaye. Cike da mamaki na. . .