Tun daga lokacin da Bashir ya yi magana a kan Maama da Salman bai sake ba. Hankalinshi kaf a kan zabe ne, daga shi har jarumar matar tashi. Kuma hankalinsu bai dawo jikinsu ba, sai da aka yi zabe, dakyar Bashir ya samu kujerarshi, a haka ma sai da aka je court. A court din ma Zahra ce ta yi ruwa ta yi tsaki, mu dai namu addu'a.
Ana cikin wannan rundunbar su Khaleel da Affan da kuma yaran Rahma su Adnan suka zo hutu, dama kuma sun saba, duk karshen shekara suke zo mana hutu.
Hankalinmu dai bai. . .